A lokacin isarta ta samu tarbe daga shugaban karamin ofishin jadancin Indonesia abirnin Jidda da kuma wasu jami'a na gwamnatin saudiyya.
Matar ta nuna farin cikinta maras misiltuwa a lokacin da ta isa birnin na Jidda, inda take ganin lallai Allah madaukakin sarki ya cika mata gurinta na sauke faralin hajji.
Ta ce dukkanin gajiyar da take a cikin jikinta ta fice a lokaci guda bayan isarta birnin na Jidda.