IQNA

Wasiyoyi 3 Na Uwar Muminai Sayyida Khadijah (RA) Ga Manzon Allah (SAW)

23:23 - April 23, 2021
Lambar Labari: 3485838
Tehran (IQNA) Sayyida Khadijah amincin Allah ya tabbata a gare ta, ta yi wa mijinta manzon Allah (SAW) wasiyoyi guda uku.

A shekara ta goma bayan aiko manzon Allah (SAW) shekaru uku kafin hijira zuwa Madina, Uwar muminai Sayyidah Khadijah ta karba kiran ubangiji madaukakin sarki.

Kafin rasuwarta, Sayyida Khadijah amincin Allah ya tabbata a gare ta, ta yi wa mijinta manzon Allah (SAW) wasiyoyi guda uku kamar haka:

1 - Manzon Allah ya rika yi mata addu'a ta alhairi

2 - Ya rufe ta hannunsa (mai albarka) a cikin kabari, kafin nan kuma ya fara shiga cikin kabarin sannan ya saka gawarta a ciki

3 - Ya saka abayar da ke jikinsa a lokacin da aka saukar masa da wahayi a kan likkafaninta

3966582

 

 

Abubuwan Da Ya Shafa: wahayi Sayyida Khadijah
captcha