A shekara ta goma bayan aiko manzon Allah (SAW) shekaru uku kafin hijira zuwa Madina, Uwar muminai Sayyidah Khadijah ta karba kiran ubangiji madaukakin sarki.
Kafin rasuwarta, Sayyida Khadijah amincin Allah ya tabbata a gare ta, ta yi wa mijinta manzon Allah (SAW) wasiyoyi guda uku kamar haka:
1 - Manzon Allah ya rika yi mata addu'a ta alhairi
2 - Ya rufe ta hannunsa (mai albarka) a cikin kabari, kafin nan kuma ya fara shiga cikin kabarin sannan ya saka gawarta a ciki
3 - Ya saka abayar da ke jikinsa a lokacin da aka saukar masa da wahayi a kan likkafaninta