Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, Rafe Alamiri fitaccen makarancin kur'ani mai tsarki dan kasar Iraki ya karanta ayar Ghadir wato aya ta 67 daga surat Ma'idah.
Ayar tana cewa; Ya kai wannan manzo ka isar da abin da aka saukar a gare ka, idan ba ka yi ba, tamkar ba ka isar da sakonsa ba ne, Allah zai kiyaye daga mutane.